:
Breaking News

YSU Za Ta Mayar da Dasa Itace Sharadin Kammala Karatu

top-news
https://ngazargamuexpressnews.com.ng/public/frontend/img/header-adds/adds.jpg

Jami’ar Jihar Yobe (YSU), Damaturu, ta bayyana shirin sanya dasa itace da kula da muhalli cikin sharuddan da ɗalibai za su cika kafin kammala karatunsu.


Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Muhammad Tahir, ne ya bayyana hakan a yayin ƙaddamar da shirin dasa itatuwa na shekarar 2026, wanda Sashen Gandun Daji da Kula da Namun Daji na Faculty of Agriculture ya shirya.

Shirin mai taken “Greening Our Faculty for a Sustainable Future” na da nufin ƙarfafa al’adun kare muhalli da kuma tabbatar da dorewar muhalli a cikin jami’ar.

Farfesa Tahir ya ce, bisa sabon tsarin da ake shirin bullo da shi, za a bukaci kowane ɗalibi ya dasa aƙalla itace guda ɗaya tun daga lokacin da ya samu gurbin karatu har zuwa lokacin da zai kammala.

Ya bayyana cewa ɗalibai na iya kasancewa wajibi su gabatar da shaidar cewa sun dasa tare da kula da itacen da suka dasa, kafin a ba su takardar shaidar kammala karatu.

A cewarsa, manufar shirin ba wai kawai kare muhalli ba ce, har ma da gina ɗabi’ar ɗaukar nauyi da kula da muhalli a tsakanin ɗaliban jami’ar.

Mataimakin Shugaban Jami’ar ya bayyana dasa itatuwa a matsayin muhimmin abu ga ɗan Adam, dabbobi da muhalli, yana mai cewa itatuwa na taimakawa wajen rage zaizayar ƙasa da ambaliyar ruwa ta hanyar shan ruwa mai yawa.

Ya kuma yaba wa shugaban sashen bisa sauraron ra’ayoyin masu ruwa da tsaki da kuma shirya wannan shiri.

Farfesa Tahir ya umarci Sashen Gandun Daji da Kula da Namun Daji da ya haɗa gwiwa da Directorate of Works and Physical Planning wajen shirya gasar dasa itatuwa ta shekara-shekara tsakanin sassa da faculties na jami’ar.

Ya kuma yi alkawarin cewa jami’ar za ta samar da lambobin yabo ga faculty ko sashen da ya fi ƙoƙari wajen dasa da kula da itatuwa, domin ƙarfafa ɗalibai da ma’aikata su ci gaba da shiga shirin.

Tun da farko, Shugaban Faculty of Agriculture, Dakta Jibril Yerima, ya yaba wa ɗaliban da suka ƙaddamar da shirin, Mohammed Mohammed da Hauwa Damagum, waɗanda dukkansu ɗaliban mataki na 300 ne a Sashen Gandun Daji da Kula da Namun Daji.

Ya kuma gode wa Manajan Shirin North East Arid Zone Development Programme (NEAZDP), Dakta Mulima Mato, bisa gudummawar kayan aikin gandun renon itatuwa da kayan dasa itatuwa da aka samar domin shirin.

Haka kuma, ya yaba wa Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Gudanarwa na Green City Garden, Ahmad Disa, bisa tallafin da ya bayar wajen ganin shirin ya yi nasara.

A nata jawabin godiya, Shugabar Sashen Gandun Daji da Kula da Namun Daji, Dakta Rabi Saleh, ta gode wa Mataimakin Shugaban Jami’ar da hukumar jami’ar bisa goyon bayan da suka bayar.

Ta ce shirin wata alama ce da ke nuna ƙudurin Jami’ar Jihar Yobe na inganta kula da muhalli da kuma tabbatar da dorewarsa.

An kammala bikin ne da Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Muhammad Tahir, ya dasa itace ta farko, lamarin da ya nuna a hukumance ƙaddamar da shirin dasa itatuwa na YSU na shekarar 2026.

https://ngazargamuexpressnews.com.ng/public/frontend/img/header-adds/adds.jpg

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *